Skip to main content

Abba kyari yayi watsi Da Umurnin Da Buhari Ya Bada akan Sauke Jakadun Kasar waje


Sahara Reporters ta kawo rahoto cewa wasu Jakadun Najeriya da su ka zarce shekarun ritaya su na cigaba da aiki tarna e da karbar alawus da kudin aiki na miliyoyin daloli wanda ya sabawa dokar aiki. Wata majiya daga fadar shugaban kasa ta bayyana cewa shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasar, Malam Abba Kyari, shi ne ya yi watsi da umarnin shugaba Buhari na dakatar da Jakadun daga aiki.

Jaridar ta ce akwai akalla Jakadu 25 na Najeriya da ya kamata a ce sun yi ritaya tun a tsakiyar shekarar 2018, sai dai har yanzu sun yi kememe sun cigaba da zama a ofis su na karbar albashi da alawus. Daga cikin Jakadun kasashen da ya kamata a ce sun dawo gida akwai Jakadun Morocco, Kamaru, Kuba, Austriya, Kenya, Beljika, Mali, Indonesiya, Filifins, Sanagal, Hungary, da na Jamhuriyyar Czech.



 Akwai Jakadun Najeriya masu uwa a gidin-murhu da su ke rike da mukaman na su duk da sun isa shekaru 60 a Duniya ko kuma sun yi akalla shekaru 35 su na aiki a dalilin kusanci da Malam Abba Kyari. A Disamban 2018, Ministan harkokin wajen Najeriya a lokacin, Geoffrey Onyeama, ya gana da shugaban kasa Buhari a game da yi wa Jakadun kasar ritaya, kuma ya samu amincewar shugaban kasar.

Daga baya Ministan ya aika takarda a madadin shugaban kasa Buhari ga wadannan Jakadu su ajiye aiki. Daga baya babban Hadimin shugaban kasa, Abba Kyari ya kyale wadannan Jakadu na-kusa shi a ofis. Rahotannin sun nuna cewa babban dalilin da ya sa a ka bar wadannan Jakadu da wasu sababbi da aka nada a bakin aiki shi ne kusancin su da COS Abba Kyari da kuma shugaban NIA na kasa.

® Legit

Comments

Popular posts from this blog

Kaifin basira da magunguna 4 da kwallon kankana ke yi a jikin dan Adam

Kankana ta kasance daya daga cikin 'ya'yan itatuwa mafi shahara a doron kasa kuma mutane da dama su kan yi santi kwarai yayin kwankwadar ruwanta musamman wadanda kwayoyin halittun su masu bambance dandano ke aiki kwarai. A yayin da kankana ta kasance cikin dangin itatuwa da ake kiransu 'ya'yan duma, 'ƙwallayen cikin da sun ƙunshi sunadarai masu tarin alfanu da kuma tasiri wajen inganta lafiyar jikin dan Adam. Sai dai kash da yawan mutane su kan watsar da ƙwallon kankana a sakamakon rashin sanin muhimmancin su wajen inganta lafiyar su. Wadannan ƙwallaye da kankana ta kunsa suna da arzikin sunadarai da suka hadar da fatty acids, proteins, minerals (magnesium, poatssium, manganese, iron, zinc, phosphorus, copper), vitamin B (thiamine, niacin, folate) da kuma calories.  Bincike ya tabbatar da cewa, ana amfani da ƙwallayen kankana a matsayin abinci a yankunan nahiyyar Asia da kuma wasu yankunan daular Larabawa ta Tsakiya inda ake gasa su kuma kwadanta da ganyayya...

MUSIC : Ali Jita - Mairo Almakura (Giwa)

Wannan wata sabuwa waka ce da ali Jita ya rerawa matar Tanko almakura wanda tayi kyau sosai. Wanda shine munka kawo muku domin saurarenku. DOWNLOAD MP3 Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com