Skip to main content

INEC Ta Tsayar Da Ranar Bawa Ganduje Da `Yan Majalisun Jiha Takardun Shaidan Cin Zabe

Shugaban wayar da kan masu zabe na INEC reshen jihar Kano, Mallam Muhammad Garba Lawal ya ce za a bawa zababen gwamnan jihar Kano, Dr Abdullahi Umar Ganduje, mataimakinsa Nasiru Yusuf Gawuna da ‘yan majalisun dokokin 40 takardan shaidan lashe zabe a ranar Laraba na mako mai zuwa.

Shugaban sashin wayar da kan masu zabe da watsa labarai na INEC, Garba Lawal ne ya bayyana hakan yayin zantawar da ya yi da manema labarai a ranar Juma’a 29 ga watan Maris.

Garba ya ce ana sa ran kwamishinan INEC na kasa mai kula da jihohin Kano, Jigawa da Katsina, Injiya Abubakar Nahuche ne zai gabatar da takardun shaidan lashe zaben ga zababun shugabannin.

Ganduje da sauran zabaun ‘yan majalisun dokokin jihar Kano 40 za su karbi takardun shaidan lashe zabe a ranar Laraba

Jam’iyyar APC ta lashe kujeru majalisar dokokin jihar 27 cikin 40 yayin da jam’iyyar adawa ta Peoples Democratic Party (PDP) ta lashe kujeru 13.

Gwamnan jihar mai ci yanzu kuma zababen gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya ci galaba a kan abokin fafatawarsa na jam’iyyar PDP Abba Kabiru Yusuf da ratar kuri’u 8,982.
Baturen zabe na jihar Farfesa Bello B Shehu ya sanar da cewa Ganduje ya lashe zaben ne bayan an gudanar da zaben rabar gardama a jihar.

A jawabinsa da ya yi na samun nasara, Dr. Abdulllahi Umar Ganduje ya yi alkawarin cigaba da ayyukan da ya fara kuma ya ce zai yiwa kowa adalci a jihar.

Comments

Popular posts from this blog

Kaifin basira da magunguna 4 da kwallon kankana ke yi a jikin dan Adam

Kankana ta kasance daya daga cikin 'ya'yan itatuwa mafi shahara a doron kasa kuma mutane da dama su kan yi santi kwarai yayin kwankwadar ruwanta musamman wadanda kwayoyin halittun su masu bambance dandano ke aiki kwarai. A yayin da kankana ta kasance cikin dangin itatuwa da ake kiransu 'ya'yan duma, 'ƙwallayen cikin da sun ƙunshi sunadarai masu tarin alfanu da kuma tasiri wajen inganta lafiyar jikin dan Adam. Sai dai kash da yawan mutane su kan watsar da ƙwallon kankana a sakamakon rashin sanin muhimmancin su wajen inganta lafiyar su. Wadannan ƙwallaye da kankana ta kunsa suna da arzikin sunadarai da suka hadar da fatty acids, proteins, minerals (magnesium, poatssium, manganese, iron, zinc, phosphorus, copper), vitamin B (thiamine, niacin, folate) da kuma calories.  Bincike ya tabbatar da cewa, ana amfani da ƙwallayen kankana a matsayin abinci a yankunan nahiyyar Asia da kuma wasu yankunan daular Larabawa ta Tsakiya inda ake gasa su kuma kwadanta da ganyayya...

MUSIC : Ali Jita - Mairo Almakura (Giwa)

Wannan wata sabuwa waka ce da ali Jita ya rerawa matar Tanko almakura wanda tayi kyau sosai. Wanda shine munka kawo muku domin saurarenku. DOWNLOAD MP3 Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com